News
Shugaban Tinubu Zai Gana Da Ƙungiyoyin Ƙwadago Kan Mafi Ƙarancin Albashi
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Za a sake yin zama tsakanin Shuagaba Bola Ahmed Tinubu da ƙungiyoyin kwadago kan batun mafi karancin albashi ga ma’aikata.
Jaridar ‘Tribune’, ta ruwaito cewa wani babban jami’in NLC ya ce Tinubu ya gayyaci wakilan ƙungiyoyin zuwa fadar shugaban ƙasa da ke Abuja domin tattaunawar.
Sanata Kawu Sumaila Ya Shigar Da Kuduri Domin A Raba Jihar Kano Gida 2
A ranar Alhamis ne za a gudanar da zaman inda ƙungiyoyin NLC da TUC suna kan bakansu na cewa 250,000 suke buƙatar ya zama sabon mafi ƙarancin albashi ga ma’aikatan.
A kwanakin baya ne gwamnatin tarayya ta ce Naira 62,000 kawai za ta iya biya inda ake fatan a zaman a samu maslaha a tsakanin ɓangarorin biyu da za a yi a gobe Alhamis
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
