News
Da Dumi-Dumi Yan sanda sun kama wasu da laifin siyar da tallafin abinci da gwamnatin tarayyar ta bayar
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Jami’an hukumar tsaro ta farin Kaya ta DSS sun kama wasu da ake zargin sun karkatar da shinkafar da gwamnatin Najeriya ta tura dan a raba wa talakawa a jihar Jahar Katsina sama da buhu 2000
Jami’an sunce sun kama mutanan ne cikin daren ranar Larabar nan a babbar kasuwar birnin Katsina, inda suka samu shagunansu cike da shinkafar
Sai dai Kuma Hukumar ta zargin wasu daga cikin jamia,n gwamnatin jihar da hannu wajan karkatar da shinkafar
idan ba,a mantaba gwamnatin tarayyar ta turawa kowacce jiha dake kasar tallafin gudunmawar kayan abinci domin rage radadin halin da talakawa suke ciki
Advertisements
