Connect with us

News

Zanga-Zanga: Yakamata shugaban ƙasa ya yiwa ƴan Najeriya cikakken jawabi  – CUPP

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

Gamayyar jam’iyyun siyasa ta CUPP ta caccaki shugaban ƙasa Bola Tinubu kan abinda ta bayyana da ɗabi’ar ko-in-kula game da zanga zangar da ake yi game da tsadar rayuwa.

Advertisement

 

Gamayyar ƙungiyoyin sun bayyana tsarin shugabancin Tinubu a matsayin mafi muni wanda ya jefa kasar nan cikin mummunan hali.

Advertisement

 

A wata sanarwa da mai magana da yawun gamayyar jam’iyyun, Mark Adebayo, ƙungiyar ta ce maimakon shugaba Tinubu yayiwa yan kasa jawabi kai tsaye sai ya bari makusantansa na bayanai na fusata yan Najeriya.

Advertisement

 

Sanarwar ta ce “A yayin da ake yin zanga-zanga a fadin kasa, shugaban kasa yana ganin ba zai iya yiwa yan kasa jawabi kai tsaye ba. Sai dai ya zabi sanya jami’ansa na kalaman fusata yan Najeriya”.

Advertisement

 

Jam’iyyun sun ce kamata yayi shugaban kasar yayiwa ƴan Najeriya jawabi tare da sassautawa al’umma.

Advertisement

PUNCH

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending