News
Zanga -Zangar matsin rayuwa bawai iya Nigeriya bace ke fama da mashassharar tattalin Arziki- Dr Abdullah Umar Ganduje
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Shugaban jam’iyyar APC na kasa Dr Abdullahi Umar Ganduje yace halin zanga-zangar adawa da wasu kudurorin gwamnati ba wai iya Kasar Nigeria bane kawai
Ganduje ya bayyanan haka ne a jiya laraba bayan karbar bakuncin wasu mazauna Kasar Amurka kan zanga-zangar matsin rayuwa dake cigaba da gudana a fadin Kasar
Jaridar daily Trust ta rawaito Shugaban APC yace dukkan kasashen dake fuskantar mashasharar tattalin na fuskantar matsi lamba daga al’ummar su na Yau da Kullum
Ganduje ya kara da cewa Tinubu ya karbi kasar ne a gabar da take da tarin matsaloli wanda yake bukatar dora kasar bisa gwadabe da hakan Zai inganta rayuwar Yan Nageriya
Yan Nigeria dai da dama na kokawa da wasu matakan gwamnatin tarayya da suka jawo hauhawar farashin kayayyaki da sauran matsaloli rayuwar inda aka alakanta hakan duk sabida cire tallafin man fetur
