Connect with us

Business

Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Published

on

Matatar Man Dangote ta zargi hukumar NUPRC da gazawa wurin gudanar da ayyukanta

SAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Advertisement

Ministan kudi kuma mai kula da tattalin arzikin Nijeriya Wale Edun, ya ce gwamnatin tarayya za ta fara sayar da danyen mai ga Dangote da sauran matatun man kasar nan a farashin Naira daga ranar 1 ga Oktoba, 2024.

Ana Tsare Da Masu Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa Fiye Da 1000 A Najeriya

Ministan ya bayyana hakan ne a ranar Litinin a taro na biyu na taron kwamitin aiwatarwa kan batun sauya farashin sayar da danyen mai zuwa Naira da shugaba Bola Tinubu ya kafa.

Advertisement

Sanarwar ta ce, an kuma samar da sabbin bayanai kan matatun mai na Fatakwal da Dangote, inda ake sa ran za a samu karin yawan man da ake samarwa daga watan Nuwamba na shekarar 2024. Sai dai, sanarwar ba ta bayyana lokacin da matatar man Fatakwal za ta fara aiki ba.

Kamfanin man fetur na Nijeriya (NNPCL) ya dage ranar fara aikin matatar mai ta Fatakwal a karo na shida tun bayan da Mele Kyari ya zama shugaban kamfanin.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending