Connect with us

News

Gwamnatin Tarayya Ta Bankaɗo Mutum 21,600 Da Ke Amfani Da Shaidar Kammala Digiri Na Boge A Najeriya 

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa akwai akalla mutum 21,600 da aka ɓankaɗo dake ɗauke da shaidar kammala digirin boge a faɗin Najeriya.

Mafi yawan ɗaliban dai sun samo waɗannan Satifiket ne daga Jami’o’in kasashen Togo, Benin da wasu jami’o’i dake kasashen waje.

Hukumar Haraji Ta Nemi A Samar Da Dokar Sa Ido A Kan ‘Yan Kirifto

PREMIUM TIMES ta ruwaito cewa Ministan Ilimi, Tahir Mamman ne ya bayyana hakan a lokacin da yake ganawa da manema labarai kan nasarorin da ya samu a ma’aikatar cikin shekara guda, bayan zaman sa ministan Ilimi a Abuja ranar Juma’a.

Mamman ya ce mutum 1,105 ke amfani da shaidar kammala digiri na boge daga kasar Togo.

” Akwai jami’o’i uku a kasar Togo da wasu guda 5 a Jamhuriyyar Benin, da sune muka sani sannan muka amince suna ba da shaidar kammala digiri na gaskiya.

Advertisement

Bayan haka Mamman ya ƙara da cewa a cikin shekara 1, ma’aikatar ilimi ta tarayya ta yi nasarar saka yaran da ba su zuwa makaranta akalla miliyan 4 makaranta.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending