News
Yan Bindinga Sun Sake Yin Garkuwa Da Jami’an Lafiya Mutum Biyu Suna Tsaka Da Aiki
DAGA MAHAMMAD MAHAMMAD ZAHRADDIN
Rahotanni sun tabbatar da Yan Bindinga sunyi garkuwa da wasu ma’aikatan Jinya guda Biyu a wani Asibiti dake Jihar Kaduna.
VOA HAUSA ta rawaito Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Mansir Hassan, ne ya tabbatar da faruwar lamarin inda ya bayyana cewa rashin sadarwar waya a yankin Birnin Gwari na Jihar ne ya hana mazauna yankin sanar da Jami’an ‘yan sanda game da harin.
Sai dai, ya bayyana cewar wasu jami’an ‘yan sanda na bin sawun ‘yan bindigar domin kamasu tare da kubutar da mutanen da suke garkuwa dasu.
Advertisements
