News
INNALILAHI WA INNA ILAHHIRRAJI’UN Allah Ya Yiwa Fitaccen Dan jarida Ahmad Isa Rasuwa
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Allah Ya yi wa fitaccen ɗan jaridar nan, da yayi suna wajen karance karancen litttattafan Hausa a kafafen yada labarai Ahmad Isah Koko rasuwa a yau Alhamis.
Ahmad Isah ya rasu ne bayan ya yi fama da gajeriyar rashin lafiya Kuma akesaran yi masa jana’iza a gobe Juma’a.
Marigayin ya shahara da karanta littattafan adabin Hausa a kafafen rediyo, musamman Shirin Rai Dangin Goro.
Ya kuma kasance tsohon ma’aikacin Rediyo Najeriya, kuma tsohon shugaban Sashen Hausa na Bond FM.
Muna masa Addu’ar Ubangiji Allah yajikansa da rahama yasa aljannar firdausice makoma.
Advertisements
