News
Shugaba Tinubu Da Buhari Ne Suka Jefa Najeriya Cikin Halin Yunwa Da Rashin Tsaro Da Rashin Cigaba – Obasanjo
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Tsohon shugaban kasa Chief Olusegun Obasanjo ya bayyana Najeriya a matsayin ƙasar da ta gaza sakamakon shugabancin tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari da kuma shugaba Tinubu.
Obasanjo ya ce, Tinubu da Buhari ne suka jefa Najeriya cikin halin yunwa da rashin tsaro da rashin cigaba.
Wasu Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Babban Jami’in Hukumar NDLEA
Obasanjo na waɗannan kalamai ne a yayin taron tunawa da marigayi, Chinua Achebe da ake duk shekara domin tun wa da shi wanda aka yi a jami’ar Yale da ke Amurka.
Tsohon shugaban ƙasar ya gabatar da wanj jawabi wanda aka naɗa, sannan aka kunna a wurin taron.
Haka kuma Obasanjo ya caccaki shugabanni biyu ta hanyar amfani da sunan da alumma suke kiran su da su na shaguɓe, wato: “Baba-go-slow” ga tsohon shugaban ƙasa Buhari da “Emilokan” ga Shugaba Bola Ahmad Tinubu.
“Kamar yadda za mu iya gani kuma mu fahimta, halin da ake ciki a Najeriya ya yi muni sosai. Ƙasa na daɗa lalacewa da kwatankwacin yadda ake samun ƙaruwar cin hanci da rashin tarbiyya.
Daga nan ne ake samun tashe-tashen hankula da matsalar tsaro da rarrabuwar kai da fargaba da makamantansu.
Waɗannan shugabanni biyu su ne suka jefa Najeriya Najeriya cikin mawuyacin halin a cewar shugaba Obasanjo.
