Connect with us

News

MAƘWABCI: Rikici Kan Rabon Shinkafa Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani Matashi

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Wani rikici kan rabon shinkafa ya yi Sanadiyyar mutuwar wani matashi mai suna Christian, wanda aka ce maƙwabcinsa Daniel Onyejekwe, mai shekaru 30, ya daba wa wuƙa a garin Sapele, Jihar Delta.

Advertisement

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Delta ta tabbatar da kamen Onyejekwe, wanda ake zargi da aikata kisan kai yayin hatsaniyar da ta ɓarke a lokacin rabon shinkafa a yankin Ogwanja, kan titin Boyo Road.

NDLEA Ta Kama Mutane 1,345 Da Wasu Muggan Kwayoyi A Kano

Mai magana da yawun rundunar, SP Bright Edafe, ya bayyana cewa, “Rikicin ya faru ne a yayin rabon shinkafa inda aka samu musayar yawu.

Advertisement

“Daga nan ne Onyejekwe ya yi amfani da kwalɓa ya daba wa Christian, wanda hakan ya kai ga mutuwarsa.”

Ganau sun shaida cewa bayan samun raunuka masu tsanani, wata ƙungiyar vigilante ta garin ta yi ƙoƙarin ceto Christian ta hanyar kai shi asibiti, amma likitoci sun tabbatar da mutuwarsa a lokacin da aka isa.

Advertisement

“Mun fara bincike kan lamarin, kuma muna tabbatar wa da jama’a cewa wanda ake zargi zai fuskanci hukunci daidai da abin da doka ta tanada,” in ji SP Edafe.

A halin yanzu, gawar Christian an ajiye ta a ɗakin ajiye gawa yayin da bincike kan dalilin rikicin da kuma yadda lamarin ya faru ke ci gaba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending