Connect with us

News

NDLEA Ta Kama Mutane 1,345 Da Wasu Muggan Kwayoyi A Kano

Published

on

Wasu Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Babban Jami’in Hukumar NDLEA

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Hukumar Hana sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA), reshen Jihar Kano, ta ce ta kama mutane 1,345 da ake zargi, sannan ta kuma kama wasu haramtattun kwayoyi masu nauyin kilogiram 8,430,239 a shekarar 2024.

Advertisement

Kwamandan Hukumar na jihar, Abubakar Idris-Ahmad, ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis 02 ga Janairu 2025, yayin wata hira da kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN a Kano.

Rashin Adalci Ne Babban Ƙalubalen Da Najeriya Ke Fuskanta  —Shugaban Majalisar Dattawa

Ya ce wadanda ake zargin sun hada da maza 1,301 da mata 44.

Advertisement

Idris-Ahmad, ya ce haramtattun abubuwan da aka kama sun hada da hemp, hodar iblis, heroin, methamphetamine, codeine, da kwayar tramadol sama da miliyan biyar.

Ya ce rundunar ta kuma kama wasu mutane 128 da aka kama da laifuka daban-daban da suka shafi muggan kwayoyi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending