Connect with us

News

Abin Fashewa Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar  Ɗalibi Ɗaya Da Raunata Wasu A Wata Makaranta A Abuja

Published

on

FB IMG 1736181736779

DAGA NUSIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA 

Wata mummunar fashewar bam ya faru a wata makaranta da ke wata unguwa a Abuja, inda ya kashe ɗalibi ɗaya kuma ya jikkata wasu huɗu, kamar yadda waɗanda suka ga abin da ya faru su baiyyana.

Wani jami’in tsaro ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 12:00 na rana a yau Litinin, a wata makarantar Islamiyya da ke unguwar Kuchibiyu, a yankin karamar hukumar Bwari, kimanin kilomita 42 daga tsakiyar birnin Abuja.

Kotu Ta Bayar Da Belin Matar Da Tayi Barazanar Kashe Dan Shugaban Kasa Tinubu, Da Shugaban Yan Sanda

Wata majiya ta ce tawagar gaggawa da jami’an tsaro, ciki har da tawogar kwararrun jami’ai masu cire bam ta ƴansanda, sun isa wurin fashewar, yayin da aka garzaya da waɗanda suka ji rauni zuwa asibiti.

PREMIUM TIMES ta ce rundunar ƴan sanda ba ta saki wani bayani kan lamarin ba tukuna.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending