Connect with us

News

Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Da Ƙirƙirar Rundunar Tsaro Mai Ɗauke Da Makamai

Published

on

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce Babu Gudu Babu Ja Da Baya Kan Zaben Kananan Hukumomin Da Aka Shirya Yi

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta amince da wata doka da zata kafa rundunar tsaro ta jiha domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Advertisement

Bayan muhawara mai zafi kan wasu sassa na dokar, majalisar ta amince da tanadi da ke hana duk wani wanda ke cikin jam’iyyar siyasa jagorantar rundunar. Shugaban masu rinjaye na majalisar, Hon. Lawan Husaini Dala, ya bayyana cewa an yi nazari sosai kan dokar don tabbatar da cewa tana amfani ga kowane ɓangare na jihar.

Dattijo Mai Shekaru 50 Ya Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga, Sun Yi Garkuwa Da Ɗansa Da Iyalansa

Sabuwar dokar ta ba wa jami’an rundunar ikon ɗaukar makamai, cafke masu laifi da kuma hana aikata miyagun ayyuka a faɗin Kano. Dala ya tabbatar da cewa wanda zai jagoranci rundunar dole ne ya kasance ba dan wata jam’iyyar siyasa ba kuma ya fito daga Kano.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending