News
Shuhaba Tinubu Ya Taya El-Rufai Murna Cika Shekaru 65 A Duniya Duk Da Rikicin Siyasa Da’ke Tsakaninsu
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Shugaban kasa Bola Tinubu ya taya tsohon gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai murnar cika shekaru 65 a duniya, inda ya bayyana shi a matsayin “shugaba, malami, kuma dan siyasa” wanda ya yi shura akan “ƙwazo da hazaka duk da sabanin da suka samu a Siyasa.
Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ,Bayo Onanuga ya fitar a ranar Lahadi , Tinubu ya yaba da rawar da El-Rufai ya taka a matsayin wanda ya bada gudunmawa wajen kafa jam’iyyar APC da kuma gudunmawar da ya bayar wajen samun nasarar jam’iyyar a zabuka uku a jere.
“Shugaban kasa ya yaba da rawar da Mallam El-Rufai ya taka ta fafutukar da aka yi kafin kafa jam’iyyar APC da kuma gudunmawar da ya bayar wajen samun nasarar jam’iyyar a zabuka uku a jere na 2015, 2019, da 2023,” in ji sanarwar.
Tinubu ya kuma yabawa “kokarin da tsohon ministan ya yi na tabbatar da dimokradiyya; kyakkyawar hidimarsa ga al’umma, da nasiha ga matasa masu tasowa.”
