News
RAMADAN: Kada Ku Yi Amfani da Gurbatattun Kaya Wajen Bada Sadaka – Babban Limamin Jami’a
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Babban Limamin Jami’ar Jihar Legas, Farfesa Amidu Sanni, ya bukaci al’ummar Musulmi da su ci gaba da da’a, kyautatawa, da bayar da agaji yayin da aka fara azumin watan Ramadan.
Sanni ya bayyana cewa bayar da sadaka da kyautatawa ga mabukata su ne alamomin watan Ramadan, don haka yana da muhimmanci a bayar da kyauta mai kyau ba wai gurbatattun kaya ba.
Gwamnatin Tarayya Ta Zargi Shugabannin Ƙananan Hukumomi da Ƙin Buɗe Asusun Banki A CBN
Malamin ya bayyana hakan ne a wata zantawarsa da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) a Legas ranar Asabar, inda ya taya al’ummar Musulmi murnar shigowar watan Ramadan.
Ya ce Ramadan lokaci ne na tsarkake ruhi da kusanci da Allah, ba wai kawai kamewa daga abinci, sha da mu’amalar jima’i daga ketowar alfijir zuwa faduwar rana ba.
-
News4 days agoShekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
-
News6 days agoKamfanonin Bada Bashi Ne Suka Cire N1.5bn Daga Albashin Ma’aikatan Kano — SSG
-
News4 days agoDr. Muhammed Musa Zango Ya Kaddamar Da Neman Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar APC
