Connect with us

News

Yadda Matar Aure Ta Rasu A Cikin Masallaci Yayin Tafsirin Ramadan

Published

on

Matar Aure Ta Rasu A Cikin Masallaci Yayin Tafsirin Ramada

 

Wata matar aure mai suna Maman Zainab, mai shekaru 42, ta riga mu gidan gaskiya bayan da ta yanke jiki ta faɗi yayin tafsirin Ramadan a wani masallaci da ke Gawu, ƙaramar hukumar Abaji a Babban Birnin Tarayya (FCT).

Advertisement

Wani mazaunin yankin, Ismail Bala, ya shaida wa Daily Trust cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11:23 na safe a ranar Talata.

Masarautar Kano: Kotun Daukaka Kara Ta Dakatar Da Mayar Da Sanusi II A Matsayin Sarki

Maman Zainab ta bar gida cikin koshin lafiya tare da wasu mata uku daga makwabta domin halartar tafsirin Ramadan, amma yayin da take cikin masallaci, sai ta fara jin jiri da matsanancin ciwon kai.

Advertisement

Da take ƙoƙarin barin masallacin, sai ta yanke jiki ta faɗi. Duk da gaggawar kai ta asibitin Gawu Babangida, likitoci sun tabbatar da rasuwarta da zarar ta isa asibitin. Likitan da ya duba ta ya bayyana cewa ta rasu sakamakon hawan jini.

Lamarin ya girgiza jama’a a yankin, musamman mata masu halartar tafsirin Ramadan. An binne ta bisa koyarwar addinin Musulunci.

Advertisement

 

Allah ya jikanta da rahama, Ameen.

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending