Connect with us

News

Hukumar Sufurin Jiragen Ruwa Za Ta Haɗa Kai Da NDLEA Don Gwajin Ƙwaya Ga Matukan Kwale-Kwale 

Published

on

Wasu Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Babban Jami’in Hukumar NDLEA

 

Hukumar kula da sufurin jiragen ruwa a Najeriya ta bayyana cewa za ta yi aiki tare da Hukumar Yaki da Sha da Safarar Ƙwayoyi ta NDLEA domin yin gwajin ƙwaya ga matukan kwale-kwalen da ke jigilar mutane a Jihar Neja.

Advertisement

Manajan shiyyar, Akapo Adeboye, ne ya bayyana hakan a yayin wani taron wayar da kai da aka gudanar, wanda ya samu halartar ‘yan kasuwa da manoma a Karamar Hukumar Katcha.

An Kullewa Gwamna Fubara shiga Kofar Majalisar Dokokin Ribas

Jihar Neja na daga cikin yankunan da ke fuskantar yawan hadurran kwale-kwale, wanda ke haddasa asarar rayuka da dama.

Advertisement

Saboda haka, hukumar ta bayyana cewa ya zama dole a tantance kwarewar kowane direban kwale-kwale, tare da yin rajistar duk fasinjojin da ke amfani da jiragen domin inganta tsaro a tafkunan jihar.

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending