Connect with us

News

Mutum 1,010 Sun Mutu Sakamakon Hare-hare A Watan Fabrairu – Rahoto

Published

on

images 6 1 739x375

 

Aƙalla mutum 1,010 ne suka mutu a faɗin Nijeriya sakamakon hare-haren ‘yan bindiga da na jami’an tsaro a watan Fabrairu, kamar yadda rahoton kamfanin Beacon Security and Intelligence ya bayyana.

Rahoton ya nuna cewa an samu raguwar sace mutane daga 1,101 a watan Janairu zuwa 955 a Fabrairu, amma adadin mutanen da aka kashe ya ƙaru daga 991 zuwa 1,010.

Dalilin Da Ya Sa Aka Hana Gwamna Fubara Shiga Majalisar Dokokin Rivers

Daga ranar 1 zuwa 28 ga watan Fabrairu, an samu hare-hare da tashin hankali har 716, waɗanda suka haddasa satar mutane 955.

Binciken ya kuma nuna cewa mutum 592 daga cikin waɗanda suka mutu fararen hula ne, inda ‘yan bindiga suka fi kai mafi yawan hare-hare 478, yayin da jami’an tsaro suka haddasa 177.

Jihohin da suka fi fama da hare-haren sun haɗa da Katsina, Kaduna, Neja, Zamfara, Sakkwato, Borno, da Kebbi.

Advertisement

Duk da raguwar hare-haren da kashi 2.19 idan aka kwatanta da Janairu, har yanzu matsalar tsaro na ci gaba da zama barazana ga al’umma a Nijeriya.

 

 

LEADSHIP

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending