Connect with us

News

Tsananin Zafi Da Bullar Cutar Sankarau: NIMET Ta Bayyana Jihohin Da Suka Fi Fuskantar Hadari

Published

on

FB IMG 1741838727826

 

Hukumar Kula da Yanayi ta Najeriya (NIMET) ta fitar da sabon rahoto da ke nuna cewa wasu jihohin kasar za su fuskanci tsananin zafin rana a kwanaki masu zuwa, lamarin da ka iya kara yawaitar cutar sankarau.

Rahoton ya bayyana cewa jihohi 12, ciki har da Kebbi, Neja, Kwara, Oyo, Kogi, Nasarawa da Benue, na daga cikin yankunan da za a fuskanci hauhawar zafin har na tsawon kwanaki uku zuwa hudu. Haka kuma, jihohin Enugu, Anambra, Abia, Ebonyi, Cross River, Taraba, Adamawa, Filato, Kaduna, Zamfara da Sakkwato na cikin wadanda ke fuskantar barazanar karuwar zafi mai tsanani.

‎Mazauna Garuruwan Alazawa Da Gazan Sun Gudanar Alkunutu Bisa Matsalolin Da Suka Dabaibaye Yankin

A sakamakon haka, likitoci sun gargadi al’umma da su dauki matakan kariya, musamman gujewa yin ayyuka a cikin rana daga karfe 12 zuwa 3 na yamma. Haka kuma, an shawarci masu azumi da su rage yawan zama a wurare masu cinkoso domin gujewa cututtukan da ake dauka ta iska, musamman sankarau.

Ana bukatar jama’a su kula da lafiyarsu ta hanyar shan isasshen ruwa da kuma kare kansu daga hasken rana mai tsanani.

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending