Connect with us

News

Fubara Ya Musanta Zargin Yana Da Hannu A Hare-haren Da Ake Kai Wa Bututun Mai

Published

on

FB IMG 1742577050209
Dakataccen gwamnan jihar Ribas, Siminalayi Fubara

Dakataccen gwamnan jihar Ribas, Siminalayi Fubara, ya musanta zargin da gwamnatin tarayya ke masa na cewa yana da hannu a hare-haren da ake kai wa bututun mai a yankin Neja-Delta.

A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Nelson Chukwudi, ya fitar, Fubara ya bayyana cewa an alaƙanta shi da lamarin ne kawai saboda rikicin siyasa da ya dabaibaye jihar, wanda ya kai ga dakatar da shi daga kujerarsa.

Advertisement

An Kama Jarkokin Manja Cike Da Alburusai 488 A Abuja

A halin yanzu, hare-haren kan bututun mai na janyo asarar miliyoyin daloli ga Najeriya, tare da haifar da barazana ga tattalin arzikin ƙasa.

Wannan lamari na zuwa ne yayin da ake ci gaba da sukar kafa dokar ta ɓaci a jihar, matakin da majalisun ƙasa suka amince da shi domin shawo kan rikicin.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending