Connect with us

News

Kantoman Ribas Ya Dakatar Da Dukkan Masu Riƙe Da  Muƙaman Siyasa

Published

on

ibot ete ibas
Spread the love

Gwamnatin Jihar Ribas ta dakatar da duk masu riƙe da muƙaman siyasa a faɗin jihar daga aiki nan take.

Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Kantoman jihar, Manjo Janar Ibok-Ete Ibas (mai ritaya), ya fitar a daren ranar Laraba.

 Sarki Aminu Ado Bayero Ya Janye Hawan Sallah Ƙarama Saboda Dalilin Tsaro

Sanarwar ta bayyana cewa matakin ya samu ne bisa ga ikon da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bai wa Ibas.

Advertisement

Sarki Aminu Ado Bayero Ya Janye Hawan Sallah Ƙarama Saboda Dalilin Tsaro

Waɗanda abin ya shafa sun haɗa da Sakataren Gwamnatin Jihar, Shugaban Ma’aikata, dukkanin Kwamishinoni, tare da mambobin kwamitoci, hukumomi, da cibiyoyin gwamnati.

Haka kuma, dukkanin Masu Ba da Shawara na Musamman, Mataimaka na Musamman, su ma an dakatar da su.

Sanarwar ta umarci dukkanin waɗanda abin ya shafa da su miƙa ragamar aiki ga Sakatarorin ma’aikatun da suke jagoranta. Idan babu Sakatare, sai miƙa ragamar ga Babban Darakta mafi girma ko Shugaban Harkokin Gudanarwa.

Advertisement

Wannan umarni zai fara aiki daga ranar Laraba, 26 ga watan Maris, 2025.

 

 

Advertisement

 

LEADSHIP

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *