News
Ba ni da Hannu A Ƙona Majalisar Dokokin Rivers – Shugaban Ma’aikatan Gwamna Fubara
Shugaban ma’aikatan gidan gwamnatin jihar Rivers, Edison Ehie, ya musanta zargin da ake yi masa na jagorantar ƙona majalisar dokokin jihar a ranar 29 ga Oktoba, 2023.
Ehie ya bayyana hakan ne a matsayin martani ga tsohon shugaban ma’aikatan jihar, George Nwaeke, wanda ya zarge shi tare da gwamna Siminalayi Fubara da hannu a lamarin.
Gwamnan Kano: A Bayyana Masu Hannu a Kisan ‘Yan Jiharmu a Edo
A wata tattaunawa da tashar Channels, Ehie ya ce ba shi da wata alaka da abin da ya faru.
“Nima kamar kowa, kawai na wayi gari ne a ranar 30 ga watan Oktoba na samu labarin an ƙona majalisar,” in ji shi.
Ehie ya bayyana cewa ya umarci lauyansa da ya maka Nwaeke a kotu bisa zarginsa da ɓata masa suna, yana mai cewa: “Ba zan ce komai a kansa ba, amma ina fata ya shirya gabatar da hujjoji da za su tabbatar da zarginsa.”
