News
Ɓarawon Waya Yayi Sanadiyyar Mutuwar Babban Jami’in Soja A Kaduna
Wani babban jami’in soja, Laftanar Commodore M. Buba, ya rasa ransa bayan da wani da ake zargin ɓarawon waya ne ya kai masa farmaki da wuka a gadar Kawo da ke cikin birnin Kaduna.
Lamarin ya faru ne a ranar Juma’a da yamma, lokacin da jami’in ya tsaya domin gyara tayar motarsa da ta fashe, yayin da yake kan hanyarsa ta dawowa daga Jaji, inda yake karatu a Makarantar Horas da Sojoji ta Armed Forces Command and Staff College (AFCSC).
Jonathan Ya Samu Goyon Bayan Gwamnoni 22, Amma Ya Fadi – Ndume Ga Tinubu
Wata majiya ta shaida wa DAILY TRUST cewa yayin da jami’in ke cikin gyaran tayar motar, sai wani mutum da ba a san ko waye ba ya karaso inda ya nemi ya ba shi wayarsa. Sai dai jami’in soja ya ƙi amsa wannan bukata, lamarin da ya fusata mutumin, inda nan take ya ciro wuka ya soka masa a kirji.
A cewar wani jami’in sa-kai da ke kusa da wajen, Suleiman Dahiru, wanda ya shaida faruwar al’amarin, ya bayyana cewa ya yi yunkurin ceton jami’in, amma shi ma barawon ya raunata ta hanyar yanke masa hannu da wuka.
Bayan faruwar lamarin, wasu matasa da ke kusa da wajen sun taru suka cafke wanda ake zargi, inda suka yi masa dukan kawo wuka har lahira.
Jami’in sojan da aka kashe an garzaya da shi zuwa Asibitin Manaal da ke cikin garin Kaduna, amma likitoci sun tabbatar da rasuwarsa. Daga bisani, an kai gawarsa zuwa dakin ajiye gawarwaki na Asibitin 44 Nigerian Army Reference Hospital da ke Kaduna.
Da aka tuntubi wata majiya daga rundunar sojan Najeriya da ta bukaci a sakaya sunanta, ta bayyana cewa tuni jami’an tsaro da suka haɗa da sojoji da ‘yan sanda suka bazama cikin gari cikin kayan fararen hula domin gudanar da bincike da kuma cafke masu aikata laifuka.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna, ASP Mansir Hassan, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai bayyana shi a matsayin abin takaici da kuma babban rashi ga jami’an tsaro da kasa baki ɗaya.
Ya kara da cewa rundunar ‘yan sandan jihar na ci gaba da ɗaukar matakai na tsaurara tsaro a sassa daban-daban na jihar domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
