Connect with us

News

Kano Online Media Chapel Ta Taya Makwarari Murnar Nadinsa A Matsayin Shugaban Himma FM Da Ke Kano.

Published

on

Jami’an Tsaro Sun Fi Kowa Hantarar Yan Jarida

Kungiyar ‘Yan Jarida na Kafafen Sadarwar Intanet a Jihar Kano (Kano Online Media Chapel) ta taya Isma’il Yusuf Makwarari murnar nadinsa a matsayin Manajan Tashar Himma Farmers 91.1 FM da ke Kano.

A cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar, Abdulkadir Abubakar Dangambo, da sakataren kungiyar, Isiyaku Ahmed, suka fitar ranar Alhamis, kungiyar ta ce nadin ya dace da cancantar Makwarari.

Advertisement

Gwamnan Kano Ya Yabawa Hukumomin Agaji Bisa Dakile Yiwuwar Fashewar Tankar Mai A Titin Gwarzo

Sanarwar ta bayyana Makwarari a matsayin ɗan jarida mai kwazo, wanda ya ba da gudunmuwa sosai ga ci gaban kungiyar da aikin jarida gaba ɗaya.

“Ya nuna ƙwarewa da gaskiya a aikinsa. Ya kasance ɗaya daga cikin manyan ginshiƙan da suka tallafa wa ci gaban kungiyar tun farko,” in ji sanarwar.

Advertisement

Kungiyar ta ce sabuwar rawar da Makwarari zai taka a tashar Himma Farmers za ta ƙara ɗora aikin jarida a jihar Kano a kan turbar da ta dace.

Ta kuma yi masa fatan nasara a sabon matsayin da aka ɗora masa.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending