News
Gwamnan Kano Ya Yabawa Hukumomin Agaji Bisa Dakile Yiwuwar Fashewar Tankar Mai A Titin Gwarzo
Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya yaba da gudunmuwar da hukumomin bayar da agajin gaggawa suka yi, wadanda suka yi nasarar dakile yiwuwar fashewar wata tankar man fetur a hanyar BUK zuwa Gwarzo ranar Laraba.
Lamarin dai ya faru ne a kusa da mahadar sakatariyar hukumar NYSC, inda wata tankar dakon man fetur ta burma rami lokacin da take kokarin shiga gidan mai, lamarin da ya haifar da fargabar barkewar gobara a yankin.
Gwamnatin Kano Ta Taya Sabon Shugaban Hima FM Alh Isma’il Yusuf Makwarari Munar Kama Aiki
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, Gwamna Yusuf ya bayyana matukar godiya ga hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) RS1.2 Kano, hukumar kashe gobara ta tarayya, kungiyar agaji ta Red Cross ta Najeriya, da hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta Kano (KAROTA) bisa gaggarumar rawar da suka taka.
Gwamna Yusuf ya yaba da hadin gwiwa a tsakanin hukumomin wajen dakile faruwar hatsari ko Wani iftila’i.
Ya kuma yi kira ga direbobin tankar mai da masu aikin mai da su kiyaye ka’idojin kariya a lokacin da ake yin lodi da sauke kaya domin kaucewa hadurra a nan gaba.
-
News6 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News2 days ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
