Connect with us

News

“Rikici Ya Ɓarke A Istanbul Kan Wallafa Zanen Annabi Muhammad (SAW)

Published

on

FB IMG 1751398644052

Zanga-zanga mai zafi ta ɓarke a birnin Istanbul na ƙasar Turkiyya, bayan wallafa wani zanen barkwanci da ake zargin yana nuna Annabi Muhammad (SAW), wanda hakan ya janyo fushi da ƙiyayya daga Musulmai da dama.

Mujallar barkwanci ta Turkiyya mai suna LeMan ce ta wallafa zanen a ranar 26 ga Yuni, 2025. Zanen ya nuna mutane biyu suna shawagi a sararin sama, ɗaya yana cewa: “Salam aleikum, ni Muhammad ne”, ɗayan kuma ya amsa: “Alaikum Salam, ni Musa ne.”

Advertisement

Tsoffin Shugabannin PDP Sun Caccaki Gwamnatin Shugaba Tinubu

Musulmai da dama sun nuna bacin ransu, suna masu cewa wannan wasa ne da sunan Annabi Muhammad (SAW), wanda ya sabawa imanin Musulunci da ƙa’idar hana zana fuskar Annabi.

Barkewar Zanga-zanga da Arangama da ‘Yan Sanda

Advertisement

A ranar Lahadi, daruruwan masu zanga-zanga suka mamaye titunan Istanbul domin nuna fushinsu kan abin da suka kira cin mutunci ga Annabi.

‘Yan sanda sun yi amfani da barkonon tsohuwa da harsasai na roba wajen tarwatsa masu zanga-zangar, musamman a kusa da wani mashaya da ake cewa ma’aikatan mujallar ke yawan ziyarta.

Advertisement

Rahotanni sun nuna cewa mutane kusan 300 ne suka shiga wannan arangama da jami’an tsaro.

Babban lauyan jihar Istanbul ya bayar da umarnin kama wasu editocin mujallar. Ministan cikin gida, Ali Yerlikaya, ya tabbatar da cafke mai zane da wasu ma’aikata uku.

Advertisement

Haka kuma, jami’an tsaro sun mamaye ofishin mujallar LeMan domin gudanar da bincike.

Gwamnan Istanbul, Davut Gul, ya bayyana cewa gwamnati ba za ta zuba ido ana cin mutuncin addinin Musulunci ba.

Advertisement

Ministan Shari’a na ƙasar, Yilmaz Tunc, ya ce: “’Yancin fadin albarkacin baki ba yana nufin a raina addini ba.”

Sai dai shugaban mujallar, Tuncay Akgun, wanda ke zaune a birnin Paris na ƙasar Faransa, ya nesanta kansa da zargin. A cewarsa, zanen bai shafi Annabi Muhammad (SAW) ba.

Advertisement

Ya ce: “Mutumin da aka kira Mohammed a cikin zanen wani musulmi ne da ya rasa ransa a harin da Isra’ila ta kai. Ba za mu taɓa ɗaukar wannan hadari na zana Annabi ba.”

A wata sanarwa da mujallar ta fitar a dandalinta na sada zumunta, ta ce: “Wannan zane ba shi da alaƙa da cin zarafin addini. An fassara shi da gangan domin tayar da hankali.”

Advertisement

Sai dai duk da wannan ƙarin haske daga mujallar, zanga-zangar na ci gaba da ɓarke a wasu sassan birnin, inda Musulmai ke ci gaba da bayyana bacin ransu da damuwa.

 

Advertisement

 

 

Advertisement

WIKKI TIMES 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending