News
Ko Tinubu Ya Nada Ɗansa Seyi Tinubu Shugaban INEC, Sai APC Ta Fadi A 2027 – Dalung
Tsohon Ministan Matasa da Wasanni, Solomon Dalung, ya bayyana cewa duk wani yunkuri da Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai yi na nada na kusa da shi a muhimman mukamai, ba zai hana jam’iyyarsa ta APC shan kaye a zaben 2027 ba.
Dalung ya fadi haka ne a wata hira da ya yi da tashar NEWS CENTRAL, inda ya ce rashin jin dadin da ‘yan Najeriya ke ciki a halin yanzu ya isa ya haifar da sauyin gwamnati a zabe mai zuwa.
“Ko Tinubu ya nada ɗansa Seyi Tinubu shugaban INEC, kuma ya nada matarsa a matsayin Babbar Alkalin Ƙoli, kuma gwamnoni 36 su koma APC, ba zai hana su faduwa ba. Jama’a sun gama gajiya,” in ji shi.
Dalung ya bayyana cewa gwamnatin Tinubu ta gaza, tana zaluntar jama’a, ta kuma mayar da fatara da yunwa da matsin rayuwa tamkar makaman yaki da talakawa.
“Zaben 2027 zai zama tsakanin ‘yan Najeriya da gwamnatin Tinubu. Gwamnatin nan ta bayyana cewa ta shiga yaki da jama’a ta hanyar tsananta rayuwa.”
Ya kara da cewa hanya daya da za a iya kawo karshen wannan tsarin ita ce jam’iyyun adawa su hade a karkashin kawancen sabuwar jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) domin kalubalantar APC a 2027.
“Lokaci ya yi da ‘yan adawa za su cire bambance-bambance su tsaya tsayin daka domin ceto kasar nan daga halin kunci da ake ciki.”
Dalung ya jaddada cewa dole ne ‘yan Najeriya su tashi tsaye, su shirya tsaf domin kada su sake fadawa hannun gwamnati irin ta yanzu da ke kara jefa su cikin kunci.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
