Connect with us

News

’Yan Sanda Sun Kama Matasa 5 Da Ake Zargi Da Kwacen Waya A Adaidaita Sahu A Kano

Published

on

Yan sanda sun cafke wani ango a ranar ɗaurin aurensa kan zargin kisan kai

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano ta kama matasa biyar da ake zargin suna kwace wa mutane wayoyi da sauran kayayyaki a cikin birnin Kano, ta hanyar amfani da babura kirar Adaidaita Sahu.

Bayanan da aka samu sun nuna cewa biyu daga cikin wadanda ake zargin an kama su ne a yankin Kofar Ruwa, bayan da jama’ar unguwar suka yi ram da su lokacin da suka yi ƙoƙarin kwace waya daga hannun wani matashi.

Advertisement

Ko Tinubu Ya Nada Ɗansa Seyi Tinubu Shugaban INEC, Sai APC Ta Fadi A 2027 – Dalung

Wani ganau ya ce, “Sun dade suna yi mana haka, amma yau an kamo su, muka tsare su har sai da ’yan sanda suka zo suka dauke su.”

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai jan hankalin jama’a da su guji ɗaukar doka a hannunsu.

Advertisement

“An kama su. Amma don Allah a daina ɗaukar doka a hannu,” in ji SP Kiyawa a wani sakon da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

A wata sabuwar sanarwar SP Kiyawa, ya tabbatar da cewa karin mutum uku da ake zargin suna cikin wata tawaga ta masu kwace waya, suma an cafke su a yankin Kano Line, tare da baburinsu kirar Adaidaita Sahu da ake zargin suna amfani da shi wajen aikata laifuka.

Advertisement

Yanzu haka dukkan su biyar suna hannun ’yan sanda, yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike a kansu kafin a gurfanar da su a gaban kotu.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending