News
Cutar Zazzabin Lassa Tayi Ajalin Mutane 151 A Najeriya – NCDC
Hukumar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Kasa (NCDC) ta bayyana cewa adadin mutanen da suka rasu sakamakon cutar zazzabin Lassa a Najeriya ya kai 151 a cikin watannin farko na shekarar 2025.
A cewar wata sanarwa da hukumar ta fitar a ranar Litinin ta hanyar shafinta na X, an tabbatar da mutum 800 da suka kamu da cutar daga farkon shekarar zuwa yanzu.
Sojojin Najeriya Sun Kama Masu Laifi 199, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda a Fagen Daga
Hukumar ta ce adadin mace-macen ya karu daga kashi 17.3 cikin 100 a shekarar 2024 zuwa kashi 18.9 cikin 100 a bana, abin da ke nuna yadda cutar ke kara kamari.
Sanarwar ta ce cikin sabbin rahotanni, an gano karin mutum 11 da suka harbu da cutar a jihohi shida, lamarin da ke kara yawan wadanda suka kamu da ita gaba daya a bana.
A cewar NCDC, jihohi biyar ne suka fi fuskantar barazanar cutar a bana, wadanda suka hada da Ondo, Edo, Bauchi, Taraba da Ebonyi, inda aka ce kimanin kashi 90 cikin 100 na masu dauke da cutar ke zaune.
Zazzabin Lassa dai na daya daga cikin cututtukan da ke yaduwa ta hanyar kashin beraye da kuma jini ko ruwa ko jikin mutum mai dauke da cutar, musamman idan ba a bi matakan kariya ba.
Hukumar ta bukaci jama’a da su kara kulawa da tsaftar muhalli, gujewa cin abinci ko sha ruwa daga wurare marasa tsafta, tare da kai rahoton duk wani wanda ke nuna alamun cutar cikin gaggawa.
-
News2 days ago
Wani Matashi Mai Shekaru 18 Ya Rasa Ransa Bayan Fadawa Cikin Ruwa A Kano
-
News2 days ago
Kaduna, Nasarawa, Zamfara Da Wasu Jihohi 10 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa —NiMet
-
News3 days ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
