Connect with us

News

‘Kashi 70% Na Mazabata Na Hannun Ƴan Bindiga’ – Ɗan Majalisa

Published

on

Ƴan bindiga sun kashe jami’an tsaro 13 a mazabar Adabka, ƙaramar hukumar Bukuyum ta Kudu a jihar Zamfara, a wani hari da suka kai ranar Juma’a.

Rahotanni sun ce bayan kisan, maharan sun hana jami’an tsaro da na ceto shigar wurin domin kwashe gawarwakin.

Ƙungiyar ASUU na shirin sake tsunduma yajin aiki

Ɗan majalisar jihar mai wakiltar Bukuyum ta Kudu, Hamisu A. Faru, ya shaida wa BBC Hausa cewa al’ummar yankin sun shiga cikin halin tsoro da tashin hankali bayan kisan.

“Musamman ganin waɗanda suke taimaka musu wajen kariya ne aka kashe. Ka ga ke nan me ya rage? Sai gudun hijira. Dama tuni wasu sun gudu zuwa Zuru,” in ji shi.

Faru ya bayyana cewa kusan kashi 70 cikin 100 na mazabar Bukuyum ta Kudu na ƙarƙashin ikon ƴan bindiga.

Ya roƙi gwamnatin tarayya da ta gaggauta tura jiragen yaƙi domin luguden wuta a dazukan da ake zargin maharan ke fakewa.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending