Connect with us

News

An kama mutum 288 kan zargin tayar da hargitsi a zabukan cike gurbi a Kano

Published

on

1755346528285

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kano ta ce ta kama mutum 288 bisa zargin tayar da hargitsi a yayin da ake gudanar da zaɓukan cike gurbi a wasu mazaɓu na Jihar.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan Nijeriya reshen Jihar Kano Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar.

Kano: Makaranta Ta Maye Gurbin “Sign Out” Da Bikin Yaye Dalibai Mai Cike Da Ilmantarwa Da Fadakarwa

Ya ce mutanen kama suna ɗauke da muggan makamai, ciki har da bindigogi da aka yi a gida da wuƙaƙe da adda da sauransu.

A ranar Asabar ɗin nan ne ake gudanar da zaɓukan cike gurbi a mazaɓu goma sha shida a jihohi 13 – Adamawa, Anambra, Edo, Enugu, Jigawa, Kaduna, Kano, Kogi, Neja, Ogun, Oyo, Taraba da Zamfara.

Sai dai fafatawar tana yin zafi a jihohi irin su Kano da Kaduna sakamakon mummunar adawar da ke tsakanin wasu manyan ‘yan siyasar jihohin.

A Jihar Kano inda Jam’iyyar NNPP take mulki, an ja zare tsakaninta da Jam’iyyar APC wadda aka kayar a zaɓen shekarar 2023.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending