News
’Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 13 Yayin Sallar Asuba A Katsina
Gwamnatin Jihar Katsina ta tura ƙarin jami’an tsaro zuwa ƙaramar hukumar Malumfashi, bayan wasu ’yan bindiga sun kai hari suka kashe mutane 13 da ke cikin masallaci yayin sallar Asuba a ranar Talata.
Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na jihar, Dr. Nasir Mu’azu, ya tabbatar da aukuwar lamarin ga manema labarai a Katsina.
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Kara Albashin Masu Rike Da Mukaman Siyasa
A cewarsa, harin na ramuwar gayya ne, sakamakon yadda al’ummar yankin suka taɓa kare kansu daga farmakin ’yan bindiga a baya.
Dr. Mu’azu ya ce an riga an tura jami’an tsaro domin tabbatar da tsaro da dawo da zaman lafiya a yankin.
Ya kuma bayyana cewa gwamnatin jihar na jajantawa iyalan waɗanda abin ya rutsa da su, tare da tabbatar musu da cewa za ta ci gaba da tallafa wa al’umma wajen ƙarfafa yaki da ’yan ta’adda.
-
News21 hours ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
-
News1 day ago
Ana Zargin Matar Aure Da Shaƙe ’Yar Kishiyarta Mai Shekara 3 Har Lahira
-
News6 days ago
KANO: Yara 24 Da Ake Tuhuma Da Laifi Sun Amfana Da Shirin Gyaran Tarbiya Maimakon Hukuncin Kotu A Watan Yuli
