News
Shugaban Kamfanin Sagama Homes Alh. Ali Nuhu Ya Zama Jagoran Matasan Arewa
Gamayyar kungiyoyin Matasa a Arewacin Najeriya sun kai ziyara ta musamman ga shugaban kamfanin SAGAMA Construction Ltd, SAGAMA Homes(Baban kamfanin gine gine da dlilacin gidace a tarayyar na Najeriya) Alhaji Ali Nuhu, a jihar Kano.
Ziyarar ta gudana kar kashin Jagorancin Comr. Aliyu Abdul Garo, da Fatima Joel Ajemasu, inda kungiyoyin suka mika shaidar girmamawa da yabo bisa irin gudunmawar da Alh. Ali Nuhu ke bayarwa wajen tallafawa matasan Arewacin Najeriya.
Shugabannin gamayyar kungiyoyin sun bayyana cewa manufar wannan ziyara ita ce nuna godiya da yabo bisa irin kokarin da shugaban kamfanin SAGAMA Homes ke yi wajen karfafawa matasa ta hanyar samar da ayyukan yi, horas da Matasa, da kuma inganta ci gaban tattalin arziki a yankin Arewa.
Sun kuma bayyana cewa irin wannan jajircewar ‘Yan kasuwa masu kishin kasa yana da matukar tasiri wajen gina al’umma mai karko, tare da karfafa zumunci da hadin kai tsakanin shugabanni da matasa.
Kungiyoyin sun yi addu’ar Allah ya kara daukaka kamfanin SAGAMA Construction tare da ba shi ikon ci gaba da gudanar da ayyukan alheri da taimako ga matasan Arewacin Najeriya da kasa baki daya.
-
News22 hours ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
-
News2 days ago
Ana Zargin Matar Aure Da Shaƙe ’Yar Kishiyarta Mai Shekara 3 Har Lahira
-
News6 days ago
KANO: Yara 24 Da Ake Tuhuma Da Laifi Sun Amfana Da Shirin Gyaran Tarbiya Maimakon Hukuncin Kotu A Watan Yuli
