Connect with us

News

Shugaban Ghana Ya Tsige Alkalin Alkalan Kasar

Published

on

71006582 803

Shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama ya tsige babbar alkalin alkalan kasar bayan wani bincike da aka gudanar ya same ta da laifin amfani da ofishinta ta hanyoyin da basu dace ba.

Gertrude Araba Torkonoo, mai shekaru 61, mace ta uku da ta shugabanci babbar kotun Ghana, an dakatar da ita daga mukamin da ta dare tun a shekarar 2023 bayan an shigar da kara a kanta.

Advertisement

Jami’an ‘Yan Sanda Sun Kama Mutum Biyu Da Bindigar GPMG, Harsashi 1,295 A Katsina

Shugaba John Mahama ya kafa wani kwamiti mai mutane biyar karkashin wani alkalin kotun kolin domin gudanar da bincike kan korafe-korafen da suka hada da zargin karya bayanan shari’a da kuma karkatar da kudaden al’umma.

Hukumar ta gano cewa an kafa dalilan aikata laifukan da ake zarginta an kuma ba da shawarar tsige ta daga mukaminta, in ji sanarwar da fadar shugaban kasar ta fitar.

Advertisement

Wannan dai shi ne karon farko da aka binciki wani alkalin alkalai a Ghana tare da kora. Mahama, wanda ya hau karagar mulki a watan Janairu, ya sha alwashin magance cin hanci da rashawa a kasar dake yammacin Afirka.

 

Advertisement

DW

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending