News
Jihar Kano Ta Saka Ranar Komawa Makarantun Firamare Da Sakandire
Gwamnatin Jihar Kano ta fitar da jadawalin da ke nuna ranakun da za a koma makarantu na firamare da sakandare a fadin jihar domin fara sabon zangon karatu na shekarar 2025/2026.
A wata sanarwa da Daraktan Wayar da Kai na Ma’aikatar Ilimi, Malam Balarabe Abdullahi Kiru, ya sanya wa hannu, makarantun kwana za su koma a ranar Lahadi, 7 ga Satumba, 2025, yayin da Sauran Makarantun za su fara karatu a ranar Litinin, 8 ga Satumba, 2025.
Sanarwar ta bukaci iyaye da masu kula da yara da su dauki wannan jadawalin da muhimmanci tare da tabbatar da ganin ’ya’yansu sun koma makaranta a kan lokaci. Haka kuma ta gargadi dalibai da za su yi sakaci cewa za a dauki matakan ladabtarwa a kansu.
Da Katin Zabe Zaku Iya Sauya Shugaba, Ku Zabi Wanda Kuke So – Inji Gwamnan Nasarawa
Kwamishinan Ilimi na jihar, Dakta Ali Haruna Makoda, ya yi fatan alheri ga malamai da dalibai a sabon zangon karatu, tare da jaddada cewa ma’aikatar za ta ci gaba da gudanar da bincike da sintiri domin tabbatar da halartar malamai da ingancin darussa.
