News
Jami’an Ƴan Sanda Sun Cafke Masu Fashi Uku A Kano, Sun Gano Motar Da Aka Sace A Abuja
Rundunar ƴan sanda ta jihar Kano ta kama wasu mutum uku da ake zargi da fashi da makami tare da gano wata mota kirar Toyota Corolla S, 2014 model da aka sace a Abuja.
Wadanda ake zargin su ne Ismail Imran mai shekaru 20, Abdulaziz Yahaya mai shekaru 31 da Musa Ibrahim Isah mai shekaru 29, dukkansu mazauna Rigasa a jihar Kaduna. An cafke su ne a ranar 6 ga Satumba, 2025, bayan wani samame da jami’an tsaro tare da hadin gwiwar sa-kai suka gudanar.
Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce binciken farko ya nuna cewa an sace motar ne a unguwar Durumi da ke Abuja a ranar 5 ga Satumba, inda masu fashin suka kai hari kan iyalan mai motar, suka kuma jikkata ɗaya daga cikinsu.
Kwamishinan ƴan sanda na Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya yaba wa jami’an da suka gudanar da aikin, yana mai cewa nasarar ta tabbatar da muhimmancin tsarin community policing.
Rundunar ta ce ana ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin, sannan za a gurfanar da waɗanda ake zargin a kotu da zarar an kammala.
Ta kuma shawarci jama’a da su rika lura tare da kai rahoton duk wani motsi da ake zargi, domin tabbatar da tsaro a jihar da ƙasar baki ɗaya.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
