News
SSANU Da NASU Za Su Tsunduma Yajin Aiki
Kungiyoyin ma’aikatan jami’o’i da ba malamai ba (NASU) da na manyan ma’aikatan jami’o’i (SSANU) sun bai wa gwamnatin tarayya wa’adin kwana bakwai kafin su tsunduma yajin aiki.
Kungiyoyin sun ce gwamnatin ta gaza cika alkawuran da ta dauka, ciki har da biyan alawus, albashin da aka rike, karin albashi, da kuma sabunta yarjejeniyar da aka kulla tun shekarar 2009.
Dalibi Ya Shafa “Super Glue” A Idanun Abokansa 8 Yayin Da Suke Barci
A cewar shugabannin kungiyoyin, tun a watan Yuni ne suka rubuta wasika ga ma’aikatar ilimi, lamarin da ya kai ga taro a watan Yuli. Amma duk da kafa kwamiti domin duba batun rabon kudin alawus na N50bn, ba a ga wani ci gaba ba.
“Mun yi hakuri, mun yi rubuce-rubuce, amma gwamnati ta yi shiru. Saboda haka, daga ranar Litinin, 15 ga Satumba, 2025, muna bai wa gwamnati kwana bakwai don ta cika alkawura. Idan ba haka ba, za mu fara yajin aiki,” in ji wasikar da kungiyoyin suka aika wa ministan ilimi.
Kungiyoyin sun ce idan suka shiga yajin aiki, jami’o’i da cibiyoyin ilimi a fadin kasar za su rufe, abin da zai sake kawo tsaiko ga harkar karatu.
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
