News
Ƙungiyar SSANU Da NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Kungiyar manyan ma’aikatan jami’o’in Nijeriya (SSANU) da kungiyar ma’aikatan ilimi (NASU) sun shirya kaddamar da zanga-zangar kwana daya a fadin kasar a ranar Alhamis, 9 ga watan Oktoba, kan gazawar gwamnatin tarayya wajen magance matsalolin da suka dade suna bukatar gwamnatin ta warware.
Sanarwar ta biyo bayan wani cikakken nazari da kwamitin hadin gwiwa na kungiyar (JAC) ya yi a ranar 6 ga watan Oktoba, bayan karewar wa’adin da aka bai wa gwamnati.
Wata Mace Ta Rabu Da Mijinta Saboda Kin Gyara Mata Wayarta Da Ta Lalace
A wata takardar da aka mika wa daukacin shugabannin NASU da SSANU na jami’o’i da cibiyoyin jami’o’i mai taken “Ƙaddamar da zanga-zanga”, JAC ta umurci dukkanin rassa da su gudanar da taron gaggawa a ranar Laraba domin zaburar da ‘ya’yan kungiyar don gudanar da ayyukan zanga-zanga a harabar jami’o’i. A yayin zanga-zangar, za a yi rubuce-rubuce a alluna, da taron manema labarai don bayyana kokensu a bainar jama’a.
Takardar mai kwanan watan Oktoba 6, ta samu sa hannun Prince Peters Adeyemi, babban sakataren NASU, da Comrade Mohammed Ibrahim, shugaban SSANU na kasa.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
