News
Shugabannin Kafofin Yada Labarai A Kano Sun Bukaci Jama’a Su Yi Rijistar Katin Zabe
Shuwagabannin kafofin yada labarai na Kano (Heads of Media Forum) sun bukaci al’umma da su tabbatar sun yi rijistar katin zabe, don inganta dimokuradiyya.
Shugaban kungiyar, Ado Sa’idu Warawa, ya yi wannan kiran ne a taron manema labarai da aka gudanar a Kano ranar Asabar. Ya ce yin rajistar katin zabe ginshiki ne na tabbatar da sahihancin zabe.
Fiye da ‘Yan Mata 2,200 Suka Fuskanci Cin Zarafi A Cikin Shekara Ɗaya A Legas — Rahoto
Warawa ya gargadi jama’a da kada su jira zuwa lokacin zabe kafin su sabunta katin su, ya kuma bukaci kowa da kowa ya ziyarci wuraren rajista, ya bi ka’idojin da aka tsara.
Ya kuma bukaci a yi amfani da kafafen yada labarai da kungiyoyin matasa wajen wayar da kan jama’a game da rajistar katin zabe, musamman ta yanar gizo.
Bugu da kari, Warawa ya yaba da ci gaban da gwamnati ke sanarwa wajen gina asibitoci, makarantu da Ababen more Rayuwa a fadin jihar.
-
News4 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Cafke Mai Safarar Makamai, Sun Kwato Harsasai 637 A Kaduna
-
News6 days ago
Jami’an NSCDC Sun Cafke Mutane Biyu Da Saniyar Da Ake Zargin Ta Sata Ce A Kano
-
News3 days ago2027: INEC Ta Tabbatar Da Ibrahim Ali Amin Little A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano A Jam’iyyar ADC
