Connect with us

News

Kogi Polytechnic Ta Dakatar Da Ma’aikata 5, Ta Kama Dalibai 4 Kan Magudin Takardun Karatu Na Jabu

Published

on

Prof. Salisu Ogbo Usman 720x430

Hukumar Kogi State Polytechnic da ke Lokoja ta ce tana gudanar da bincike kan wata ƙungiya da ake zargi da yin maguɗin takardun shaidar karatu da kuma jabun sakamako a cikin makarantar.

Rector na makarantar, Farfesa Salisu Ogbo, ne ya bayyana hakan a lokacin da yake magana da manema labarai a Lokoja.

‎Sabbin Hafsoshin Tsaro: Sanata Barau Ya Nemi Su Nuna Cikakkiyar Biyayya Ga Shugaban Ƙasa Da kuma Kundin Tsarin Mulkin Najeriya

Ya ce an dakatar da ma’aikata biyar, yayin da aka kama dalibai hudu da ake zargin suna da hannu a cikin zancen.

Farfesan ya ce binciken farko ya gano takardun shaidar ND guda 30 da aka ƙirƙira kuma aka sayar da su ga wasu mutane da nufin neman shigar HND da su.

Ya ce an gano wannan maguɗin ne bayan rahotannin leƙen asiri da kuma binciken tantancewa da sassan Admission, ICT da na tsaro na makarantar suka gudanar.

A cewarsa, akwai wasu ma’aikatan da suka haɗa kai da masu sarrafa sakamako domin shirya sakamakon ƙarya ga daliban da suka kasa jarrabawa, amma ake nuna su kamar sun kammala karatu.

Advertisement

Farfesa Ogbo ya ce irin waɗannan ayyuka suna barazana ga martabar makarantar da amincin takardunta, yana mai jaddada cewa duk wanda aka tabbatar da laifinsa zai fuskanci hukunci.

“Ba za mu lamunci wani aiki da zai bata martabar wannan makaranta ba. Za mu ci gaba da kare sahihancin takardunmu,” in ji Farfesa Ogbo.

 

 

SOLACEBASE 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending