Connect with us

News

Majalisar Dattawa Ta Bukaci Daukar Karin Sojoji 100,000 Domin Dakile Matsalar Tsaro

Published

on

An yi wata musayar wuta tsakanin sojojin Najeriya da tawagar dan ta'adda Bello Turji

Majalisar Dattawan Najeriya ta bukaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya umarci rundunonin sojin kasa su dauki karin jami’ai akalla 100,000, domin karfafa yaki da matsalolin tsaro da suka ta’azzara a fadin kasar.

Wannan bukatar ta biyo bayan kudirin da Sanata Yahaya Abdullahi daga jihar Kebbi ya gabatar, sakamakon sace dalibai 25 na makarantar sakandiren mata ta Maga da ke jihar. Sanatan ya bayyana lamarin a matsayin babban kalubale ga hukumomi, yana mai cewa hakan na iya janyo fargaba har ta kai ga dalibai mata daina zuwa makaranta.

Advertisement

Matar Da Ta Shirya Kashe Mijinta Kan Naira Dubu 400 Ta Faɗa Komar ’Yan Sanda A Kaduna

Shugaban Majalisar Dattawan, Sanata Godswill Akpabio, shi ma ya nuna damuwarsa kan yawaitar garkuwa da dalibai a makarantun kasar. Majalisar ta ce ta kafa kwamiti don binciken yadda ake tafiyar da kudaden da aka ware wa shirin kare makarantu (Safe Schools Initiative).

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending