News
Maganin Sauro Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar mutum 4 Yan Gida Daya A Kano
Wata mummunar gobara ta tashi a safiyar Laraba a unguwar Kundila Layin Baba ‘Imfosibul’, da ke cikin karamar hukumar Tarauni ta jihar Kano, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane hudu a dangi ɗaya.
Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta tabbatar da faruwar al’amarin cikin wata sanarwa da mai magana da yawunta, ACFO Saminu Yusif, ya fitar. Ya ce jami’in hukumar, HFS Abba Datti, ne ya fara bayar da rahoton gobarar da misalin ƙarfe 4:13 na safiya.
Jirgin Ruwa Dauke Da Fasinjoji 270 Ya Yi Taho-mu-Gama A Gabar Tekun Koriya Ta Kudu
A cewar hukumar, lokacin da jami’anta suka isa wurin, gobarar ta riga ta mamaye gidan mai ɗakuna biyu, falo, kicin da bandaki.
Sanarwar ta bayyana cewa gobarar ta rutsa da mutum biyar a cikin gidan – ciki har da mahaifi mai shekaru 43, Shodandi; matarsa Rafi’a, mai shekaru 30; da ‘ya’yansu mata biyu, Mardiya (3) da Yusira (shekara 1 da rabi) – dukkansu sun mutu sakamakon shakar hayaki da konewa.
Sai dai an samu nasarar ceto yaro ɗan shekara 12, mai suna Aminu Shodandi, wanda aka fitar da shi cikin hayaniya da raunuka.
Hukumar kashe gobarar ta jajanta wa iyalan da abin ya shafa, tare da yin kira ga jama’a da su ci gaba da kula da wutar lantarki, tanda, da duk wasu abubuwan da ka iya haddasa gobara musamman a wannan yanayin sanyi na hunturu.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
