Connect with us

News

Gobara Ta Lalata  Sansanin ’Yan Gudun A Borno

Published

on

FB IMG 1763803084067
Spread the love

Wata gobara ta tashi a sansanin ’yan gudun hijira na Mafa da ke Jihar Borno, inda ta lalata matsugunan wucin gadi guda 40 tare da kayan abinci da sauran kayan gida.

Kamar yadda rahoton ke nunawa cewar, lamarin ya faru ne da misalin karfe 11:20 na safiyar Laraba.

Dalilan Da Suke Kawo Sake Ƙaruwar Hare-Hare Kan Makarantu A Arewacin Najeriya ‎

An tuntuɓi hukumar kashe gobara ta tarayya da ta Jiha nan take, yayin da ƙungiyoyin sintiri ƙarƙashin jagorancin DPO na Mafa suka taimaka wajen daƙile cunkoson jama’a da kuma hana satar kayayyaki.

Daga ƙarshe rahoton da ke garin na nuna cewar an kashe gobarar ba tare da an samu rahoton raunuka ko asarar rayuka ba.

Advertisement

Har yanzu ba a tantance adadin kadarorin da suka lalace ba, kuma ana ci gaba da bincike kan musabbabin gobarar.

 

AMINIYA

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *