Connect with us

News

Dakarun Soji Sun Ceto Yan Mata 12 Da ISWAP Suka Sace A Borno

Published

on

afd00bf9 9974 4782 af6d 2b105b7d174e

Dakarun Operation Hadin Kai (OPHK) sun ceto yan mata 12 da mayakan ISWAP suka sace a Gundumar Mussa, Karamar Hukumar Askira/Uba a Jihar Borno, a cewar majiyoyin tsaro a ranar Asabar.

An sace yan matan ne ‘yan tsakanin shekara 15 zuwa 20 a ranar 23 ga Nuwamba, yayin da suke girbi a gonakin iyayensu.

Advertisement

Lamarin ya jawo far gaba a yankin, inda wasu mazauna suka tsere zuwa makwabtan garuruwa.

Majiyar tsaro ta bayyana wa zagazola makama cewa sojojin sun kammala aikin ceto cikin nasara, kuma dukkansu sun dawo lafiya.

Advertisement

Sunayen wadanda aka ceto sun hada da Fatima Shaibu (17) ,Fatima Umaru (15), Hauwa Abubakar (18), Saliha Muhammed (15), Sadiya Umaru (17), Amira Babel (15), Zara Adamu (17), Nana Shaibu (15), Zainab Musa (18), Zainab Muhammed (17), Jamila Saidu (15), Hauwa Hamidu (17)

An kai su wani wuri mai tsaro na soji domin duba lafiyarsu da yin cikakken bayaninsu kafin a mika su ga iyayensu.

Advertisement

Ceton ya zo ne a daidai lokacin da sojoji ke karfafa ayyukan su a kudancin Borno don murkushe ragowar mayakan ISWAP da ke da hannu a hare-hare da sace-sacen mutane.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending