News
Ƴan Najeriya na neman bayani kan dala miliyan 30 na samar da tsaron makarantu
’Yan Najeriya na ci gaba da neman bayani game da makomar dala miliyan 30 da aka tattara domin samar da tsaro a makarantu tun bayan sace ɗaliban Chibok a 2014, musamman ganin yadda hare-haren satar ɗalibai suka sake farfado da ƙarfi a arewacin ƙasar.
Tun bayan sace sama da ɗalibai 300 na makarantar sakandaren Chibok, hukumomin Najeriya suka kafa gidauniyar musamman don inganta tsaron makarantu, ƙarƙashin wani tsari da tsohon Firayim Ministan Birtaniya, Gordon Brown, ya tallafa masa.
Shugaba Tinubu Na Duba Yiwuwar Naɗa Janar Christopher Musa A Matsayin Sabon Ministan Tsaro
A shekarar 2014, hukumar kula da yankin Arewa maso Gabas ta tara naira biliyan 80, tare da gudunmawar:
Dala miliyan 1.5 daga ƙasar Norway
Dala miliyan 1 daga AfDB
Dala 50,000 daga shugaban bankin
Fam miliyan 1 daga gwamnatin Birtaniya
Bayan shekara guda kuma:
Switzerland ta bada dala miliyan 8
Amurka ta bada dala miliyan 2
Qatar ta bada dala miliyan 2
’Yan kasuwar Najeriya suka taimaka da dala miliyan 10
Duk da wannan tarin tallafi, satar dalibai ta ci gaba da ƙaruwa.
Binciken da jaridar The Guardian ta gudanar ya nuna cewa a cikin ’yan shekarun nan, an kai wa makarantu hari 20 a jihohi 10 na arewacin Najeriya, lamarin da ya haifar da:
Sace ɗalibai sama da 2,000
Rufe makarantu kusan 800
Kungiyar Save the Children ta ce har yanzu makarantun yankin na fuskantar barazana ta tsaro.
Babbar jami’ar da ke kula da shirin tsaron makarantu, Hajiya Halima Iliya, ta bayyana cewa gwamnati ta amince da sabon shiri na shekaru uku (2023–2026) domin gyara tsaron makarantu.
A cewar ta, za a kashe:
Naira biliyan 32.58 – 2023
Naira biliyan 36.98 – 2024
Naira biliyan 37.15 – 2025
Naira biliyan 38.03 – 2026
Ta ce shirin zai gudana ne a makarantu 48 a kowace jiha daga cikin jihohi 18 da suka fi fama da matsalar tsaro.
Kididdiga ta nuna cewa makarantu sama da 42,000 za su ci gajiyar shirin, musamman wajen samar da katange da kayan tsaro.
Sai dai har yanzu akwai makarantun sakandare 4,270 a jihohin arewa 19 da biyu a kudu da ba su da katanga.
Ga adadin jihohin da ke da mafi yawan makarantun da ke buƙatar katanga:
Bauchi – 574
Benue – 447
Kano – 500
Adamawa – 379
Jigawa – 269
Sauran jihohin sun haɗa da:
Kogi – 296
Kebbi – 203
Kaduna – 164
Filato – 159
Gombe – 161
Katsina – 145
