Connect with us

News

Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Jamhuriyar Benin

Published

on

1765101233106 1

Sojoji a kasar Jamhuriyar Benin sun kifar da gwamnati a wani juyin mulki da suka sanar a ranar Lahadi.

Sojojin sun bayyana ne a gidan talabijin na kasar inda suka sanar da tsige Shugaban Kasa Patrice Talon da kuma rushe duk hukumomin kasar.

Advertisement

Gwamnatin Taraba Ta Sassauta Dokar Taƙaita Zirga-zirga A Wasu Yankunan Jihar 

Dakarun, karkashin jagorancin Laftanar Kanar Pascal Tigiri, sun rufe iyakokin kasar da rushe jam’iyyun siyasa.

Zuwa lokacin kammala wannan labarin babu labarin halin da Shugaba Talon masi shekara 67, wanda ke kan karagar mulkin tun a 2016 yake ciki.

Advertisement

Amma ministan harkokin kasar, Olusegun Ajadi Bakari, ya ce an samu yunkurin kifar da gwamnati, amma sojoji na neman shawo kan lamarin.

Ofishin Shugaban Kasar ya sanar cewa Shugaba Talon yana cikin koshin lafiiya, kuma sojojin kasar na kokarin murkushe wasu ‘yan tsiraru da ke yunkurin juyin mulkin.

Advertisement

 

 

Advertisement

AMINIYA

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending