Connect with us

News

Gwamnatin Kano Ta Kafa Runduna Ta Musamman Da Za Ta Ke Tsaron Tashoshin Mota ‎

Published

on

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da kafa wata runduna ta musamman da za ta ke tsaron tashoshin mota da sauran wuraren taruwar jama’a a faɗin jihar.

‎Mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ne, ya bayyana hakan cikim wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi.

Babba Dan Agundi: Karramawar Digirin Girmamawa Ta Nuna Nagartaccen Shugabancin Gwamna Namadi

‎Sanarwar ta ce wannan mataki wani ɓangare ne na ƙoƙarin gwamnatin na daƙile laifuka da kuma kare jihar, musamman manyan hanyoyin shiga da fita na birnin Kano.

‎An bayyana cewa tashoshin mota na daga cikin wuraren da ake fuskantar barazanar tsaro saboda yawan zirga-zirgar mutane.

‎Rundunar ta musamman za ta mayar da hankali kan sanya ido, tattara bayanan sirri da gudanar da ayyukan tsaro tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro a tashoshin mota da sauran wurare a jihar.

‎Haka kuma za ta kula da wurare kamar gidajen mai da sauran wuraren da mutane ke taruwa.

Advertisement

‎Gwamna Abba, ya ce wannan mataki na nufin daƙile barazanar tsaro, inganta haɗin kai tsakanin hukumomin tsaro, da kuma dawo tabbatar da kwanciyar hankali a jihar.

‎Ya ƙara da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba mara wa hukumomin tsaro baya wajen kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Jihar Kano.

AMINIYA

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending