News
Babba Dan Agundi: Karramawar Digirin Girmamawa Ta Nuna Nagartaccen Shugabancin Gwamna Namadi
Darakta Janar na hukumar kula da ingancin ayyuka ta Kasa (National Productivity Centre – NPC), Dakta Baffa Babba Dan Agundi, ya taya Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar A. Namadi, murna kan digirin digirgir na girmamawa (Honoris Causa) da Jami’ar Tarayya ta Otuoke da ke Jihar Bayelsa ta ba shi a fannin Kasuwanci da Dorewa wajan kawu gaba.
A cikin wata sanarwa da ya aikewa manema labarai a ranar 14 ga Disamba, 2025, Babba Dan Agundi ya bayyana cewa an ba gwamnan karramawar ne bisa abin da ya kira nagartaccen shugabanci da jajircewa wajen tafiyar da mulki cikin gaskiya.
Shugaban Karamar Hukumar Rimin Gado Ya Kaddamar Da Aikin Gina Katafariyar Gadar Kogin Karofin Yashi
Ya ce Gwamna Namadi ya taka rawa a gyaran harkokin gwamnati, bunƙasa aikin noma, inganta ilimi, ƙarfafa matasa da kuma haɓaka tattalin arzikin Jihar Jigawa.
“Wannan karramawa tana nuna irin gudunmawar da gwamnan ke bayarwa a hidimar jama’a da kuma ƙoƙarin samar da ci gaba mai ɗorewa,” in ji Daraktan-Janar ɗin.
Babba Dan Agundi ya ce karramawar ba ta shafi Gwamna Namadi kaɗai ba, illa har da al’ummar Jihar Jigawa baki ɗaya, inda ya bayyana ta a matsayin abin alfahari ga jihar.
Ya kuma yaba wa Jami’ar Tarayya ta Otuoke bisa yadda ta karrama abin da ya kira nagarta da ƙwarewa a harkokin manufofin jama’a da shugabanci, yana mai cewa hakan na ƙarfafa sauran masu rike da muƙaman gwamnati su rungumi gaskiya da ladabi.
Daraktan-Janar ɗin ya kammala da yi wa Gwamna Namadi fatan ƙarin nasara da basira wajen ciyar da Jihar Jigawa gaba.
-
News6 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News4 days ago
Wasu Kansiloli Na Zargin Ciyaman Da Daukar ‘Yan Daba Domin Kai Musu Hari A Kano
-
News6 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
