Connect with us

News

Tsohon Babban Alkalin Alkalan Najeriya Tanko Muhammad Ya Rasu

Published

on

1765886071689
Spread the love

Tsohon Babban Alƙalin Ƙasa (CJN), Mai Shari’a Ibrahim Tanko Muhammad (mai ritaya), ya rasu a wani asibiti da ke Ƙasar Saudiyya.

Wata majiya ta tabbatar da cewa marigayin ya rasu da safiyar Talata, lamarin da ƙungiyar dalibai musulmai na fannin shari’a ta NAMLAS ta tabbatar a wata sanarwar ta’aziyya da ta fitar a Abuja ranar 16 ga Disamba, 2025.

Sai Da Buhari Ya Gasgata Cewa Ina Son Kashe Shi —Aisha Buhari

NAMLAS ta bayyana rasuwarsa a matsayin babbar rashi ga bangaren shari’ar Nijeriya da sana’ar lauya da al’ummar Musulmi da ƙasa baki ɗaya, tana mai bayyana shi a matsayin mutum mai gaskiya da tawali’u da jajircewa wajen tabbatar da adalci.

Ƙungiyar ta ce marigayin ya gudanar da aikinsa da hikima da biyayya ga doka, tare da barin kyakkyawan tarihi da zai ci gaba da zama jagora ga al’ummomin lauyoyi na gaba.

Advertisement

 

 

DAILY NIGERIAN 

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *