News
Kungiyar Mashawartan Gwamnan Kano Ta Bukaci Yan Siyasa Su Guji Kalaman Da Ka Iya Tayar Da Rikici Ko Haddasa Rarrabuwar Kai A Jihar
Kungiyar Mashawarta na Musamman ga Gwamnan Jihar Kano ta bukaci ‘yan siyasa, masu rike da mukamai da kuma magoya bayan jam’iyyun siyasa da su guji kalamai ko ayyukan da ka iya tayar da rikici ko haddasa rarrabuwar kai a jihar.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Sakataren Kungiyar, Dr. Idris Salisu Rogo, ya fitar, inda ya yi tsokaci kan yanayin siyasar Jihar Kano da ke sauyawa a halin yanzu.
Kungiyar Likitoci Za Ta Sake Tsunduma Yajin Aiki Daga Ranar 12 Ga Janairu
A cewarsa, siyasa a tsarin dimokuraɗiyya dabi’a ce mai cike da sabani, amma ya kamata a gudanar da ita bisa mutunta juna, ladabi da kishin zaman lafiya domin kare muradun al’umma.
Kungiyar ta bayyana cewa amfani da kalaman hura wuta, cin mutunci, barazana ko tona sirrin tattaunawar kashin kai na iya raunana amincewar jama’a, tare da karkatar da hankali daga manyan al’amuran shugabanci da ci gaban jihar.
Sanarwar ta jaddada cewa Gwamnan Jihar Kano shi ne jagoran gwamnati, kuma shi ke da alhakin yanke muhimman hukunci kan alkiblar siyasar jihar.
Mashawartan sun ce suna goyon bayan duk wani mataki da gwamnan zai dauka domin kare muradin Kano.
Haka kuma, Kungiyar ta tabbatar da goyon bayanta ga manufofin gwamnan da suka shafi inganta shugabanci, bunƙasa ababen more rayuwa, walwalar jama’a da sauye-sauyen da nufin inganta rayuwar mazauna Jihar Kano.
Kungiyar ta yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki da su fifita zaman lafiya, mutunta juna da muradin Jihar Kano fiye da bukatun siyasa na kashin kai.
-
News3 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News6 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News5 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
